An Ji Karar Wani Abin Fashewa a Birnin Doha na Ƙasar Qatar, Yayin da Barazanar Hari ke Kara Ƙaruwa kan Sansanonin Sojin Amurka

Rahotanni daga ƙasar Qatar sun bayyana cewa an ji ƙararrakin fashewar wasu abubuwa masu ƙarfi gaske da ake tunanin bama-bamai ne, yayin da aka ga haske sosai  a sararin samaniya a birnin Doha, babban birnin ƙasar.

Lamarin ya faru ne a lokacin da ake kara samu ƙaruwa a fargabar  da barazana kan yiwuwar kai hari ga sansanonin sojin Amurka da ke ƙasar.

Duk da cewa hukumomin Qatar ko na Amurka ba su fitar da cikakken bayani kan lamarin a hukumance ba, wannan lamari ya jefa al’umma cikin fargaba, musamman ma da yake sansanonin sojin Amurka a yankin sun kasance cikin shirin ko-ta-kwana tun bayan karuwar tashin hankali a  yankin Gabas ta Tsakiya.

Za a ci gaba da bibiyar lamarin domin samun karin bayani daga hukumomin tsaro na Amurka da kuma gwamnatin Qatar dangane da asalin abubuwan da suka faru.

Previous Post Next Post