'Yan Bindiga Sun Kashe Makiyayi, Sunyi Awon Gaba Da Shanu a Konduga, Jihar Borno

Wasu ’yan bindiga sun hallaka wani makiyayi tare da yin awon gaba da shanunsa da ba a tantance adadinsu ba a karamar hukumar Konduga ta jihar Borno.


Rahotonni
 daga majiya mai tushe ya nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 na dare a ranar Asabar, 21 ga Yuni, a cikin dajin Jewu da ke kusa da garin Jakana.

Bayanai sun nuna cewa Makiyayin da aka halaka sunana sa Mohammed Audu mai shekaru 31,  maharan sun kai masa farmaki ne a lokacin da yake kiwon dabbobinsa.

Ya samu raunin harbin bindiga, inda aka garzaya da shi Asibitin Gwamnati na Jakana, amma likitoci sun tabbatar da rasuwarsa.

Dan uwa ga marigayin, Sanda Audu, ne ya kai rahoton harin ga jami’an tsaro washe gari da safe. Ana zargin maharan sun tsere da shanun  zuwa wani wurin da ba a sani ba.

Bayan faruwar harin, sojojin Operation Hadin Kai, ’yan sanda, ’yan sa-kai (CJTF) da maharba sun kai samame yankin. tare da ziyarta wurin da lamarin ya faru, sun tattara shaidu, tare da fara  bincike don gano wadanda suka aikata wannan mummunan harin da kuma bibiyar dabbobin da suka sace.

An mika gawar marigayin ga iyalansa domin a yi masa jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tsara.

Previous Post Next Post