Hadin Kai Tsakanin Masu Ruwa Da Tsaki ne Zai Rage Matsalar Ambaliyar Ruwa da Sauran Iftila'i

Tsohon shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Kano SEMA Kuma sarkin fadar Karaye, Comrade Sale Aliyu Jili, ya ce samar da  haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a hankar iftila'i, ne zai kawo ƙarshen matsalar ambaliyar ruwa da aka fuskanta a wasu jahohi.

A zantawarsa da KRM Hausa, Comrade Jili, ya ce kafa kwamitoci na bada agajin gaggawa a Kananan hukumomi da suka yi a baya, ya taimaka ta hanyar wayar da kan al'umma musamman a Karkara, wanda hakan yayi tasiri sosai wajen nunawa al'umma illolin ambaliyar ruwa da sauransu.


Kazalika Jili, ya shawarci gwamnatin Jihar Kano kan ta karkade dokar da hukumar ta SEMA ta samar a baya domin aiwatar da ita, wanda yin hakan zai taimakawa hukumar don samu damar yin ayyukan agaji a koda yaushe.

Daga nan sai ya shawarci masu yin gine-gine akan hanyoyin ruwa da masu yin gini cikin gaggawa dasu kaucewa wannan dabi'ar domin tana daga cikin matsalolin dake haddasa rushewar gidaje a lokutan damina.

Previous Post Next Post