Aƙalla wasu da ake zargin ƴan bindiga ne guda uku sun mutu a hannun ƴan sa-kai a kauyen Garagi da ke gundumar Mayanchi a karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara.
Wannan samame na daga cikin ire-iren matakan tsaro da aka ɗauka na ƙara sanya idanu domin dakile ayyukan ta’addanci da suka addabi yankin.
Ana ci gaba da bincike domin gano asalin waɗanda aka kashe tare da tantance ko suna da alaƙa da wasu gungun masu aikata laifuka da ke kai hare-hare a sassan yankin.
Tags:
Labarai