Kotun Afirka ta Kudu ta bude sabon
bincike kan kisan gillar da aka yi shekaru 40 da suka gabata na masu fafutukar
kawar da tsarin wariyar launin fata guda hudu da wasu jami’an yansanda suka yi.
Babu wanda aka gurfanar a gaban shari’a game da kisan gillar da aka yi wa mutanen guda hudu a shekarar 1985, kuma iyalansu sun zargi gwamnati da yin katsalandan don hana ruwa gudu a shari’ar.
Malaman makarantar da aka
halaka su uku, sun hada da Fort Calata
sai Matthew Goniwe da Sicelo Mhlauli,
tare da wani ma’aikacin jirgin kasa
Sparrow Mkonto, inda aka sace su tare
da kashe yayin da suke komawa gida daga
wani taron siyasa a garin Cradock da ke kudancin kasar.
Wannan shi ne binciken
shari’a na uku game da kisan mutanen guda hudu wanda ya faru ne a
lokacin da gwamnatin masu mulkin mallaka
ke tsananta wa masu fafutukar kawar da launin fata.