Hukumomin kasar Saudiyya sun
hana fiye da mutane dubu 269, da ba su da izinin zama a kasar a  hukumance 
shiga birnin Makkah kafin fara 
aikin hajjin bana.
Wannan mataki, kamar yadda
jaridar Al Arabiya ta ruwaito a ranar Lahadi, na cikin wani yunkuri na rage
cunkoson jama’a da tabbatar da tsaro yayin aikin hajji na wannan shekara.
Ma’aikatar Cikin gida ta kasa ta bayyana cewa wannan matakin yana shafar baki da mazauna Saudiyya da ke kokarin yin hajji ba tare da samun izini ba.
An kuma saka  tara 
ta kimanin  dala  dubu  
5,  ga wadanda aka samu da aikata
lefin,  tare da yiwuwar korar su
daga  cikin  kasar. Bugu da kari hukumomin kasar sun
hukunta sama da mazauna kasar dubu 
23,000 saboda karya dokokin hajji sannan an soke lasisin masu bada
ayyukan hajji guda 400.
A wani taron manema labarai
da aka yi a Makkah, Janar Mohammed al-Omari ya bayyana wa ‘yan jarida cewa,
bisa ka’ida, Iya wadanda ke da izinin yin hajji ne aka yarda su gudanar da
aikin, ko da suna zaune a birnin makkatun mukarrama.
