Saudiyya sun hana fiye da mutane dubu 269, da ba su da izinin zama a kasar a hukumance shiga birnin Makkah kafin fara aikin hajjin bana.

 

Hukumomin kasar Saudiyya sun hana fiye da mutane dubu 269, da ba su da izinin zama a kasar a  hukumance  shiga birnin Makkah kafin fara  aikin hajjin bana.

Wannan mataki, kamar yadda jaridar Al Arabiya ta ruwaito a ranar Lahadi, na cikin wani yunkuri na rage cunkoson jama’a da tabbatar da tsaro yayin aikin hajji na wannan shekara.

Ma’aikatar Cikin gida ta kasa ta bayyana cewa wannan matakin yana shafar baki da mazauna Saudiyya da ke kokarin yin hajji ba tare da samun izini ba.


An kuma saka  tara  ta kimanin  dala  dubu   5,  ga wadanda aka samu da aikata lefin,  tare da yiwuwar korar su daga  cikin  kasar. Bugu da kari hukumomin kasar sun hukunta sama da mazauna kasar dubu  23,000 saboda karya dokokin hajji sannan an soke lasisin masu bada ayyukan hajji guda 400.

A wani taron manema labarai da aka yi a Makkah, Janar Mohammed al-Omari ya bayyana wa ‘yan jarida cewa, bisa ka’ida, Iya wadanda ke da izinin yin hajji ne aka yarda su gudanar da aikin, ko da suna zaune a birnin makkatun mukarrama.

Previous Post Next Post