NiMet ta yi hasashen za a samu guguwar iska da ruwan sama daga Litinin zuwa Laraba a jihohin Kano, Taraba, Kaduna, Gombe, Bauchi, Kebbi, Sokoto, Katsina da Jigawa.

 

Hukumar kula da yanayi ta kasa NiMet ta yi hasashen za a samu guguwar iska da ruwan sama daga Litinin zuwa Laraba a jihohin Kano, Taraba, Kaduna, Gombe, Bauchi, Kebbi, Sokoto, Katsina da Jigawa.

NiMet ta bayyana hakan ne a cikin rahoton yanayi da ta fitar a ranar Lahadi a Abuja, inda ta yi hasashen yiwuwar samun guguwar iska da ruwa a wasu sassan jihohin Taraba, Kaduna, Sokoto, Borno, Kebbi da Zamfara daga baya a ranar.

Hukumar ta kuma yi hasashen za a samu guguwar iska da ruwan sama da safe a ranar Talata a wasu sassan Kano, Zamfara, Katsina, Bauchi, Gombe, Adamawa, Borno, Yobe da Taraba.

Previous Post Next Post