Majalisar Wakilan Najeriya ta wanke ƙasar Togo daga zargin bayar da takardun shaidar kammala karatu na bogi, inda a halin yanzu zargin kacokan ya koma kan Jamhuriyar Benin, inda aka gano shaidu dake nuna yadda ake cinikin takardun kammala karatu a matakai daban daban .
Ƙarar ta kalubalanci hukuncin da Ma’aikatar Ilimi ta gwamnatin Tarayya ta yanke a bara, wanda ta haɗa ƙasashen Togo da Benin a cikin zargin bada shaidar kammala digiri na bogi, wanda hakan ya yamutsa hazo a kasar nan.
Laori ya bayyana cewa binciken diflomasiyya da Ma’aikatar Harkokin Waje ta gudanar ya tabbatar da cewa Togo ba ta da hannu a cikin lamarin, tare da ƙara jaddada ingancin cibiyoyin iliminta.
Kwamitin ya sanya ranar 10 ga watan Yulin 2025, domin ci gaba da sauraren korafin, inda a halin yanzu zata mayar da hankali kan Jamhuriyar Benin kadai.