Majalisar Masarautar Gaya da ke cikin Karamar Hukumar Gaya ta tuɓe rawanin sarautar Wazirin Gaya daga hannun tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji.
Alhaji Bello ya bayyana cewa matakin ya nuna yadda masarautar ke dagewa wajen kare mutunci, kima da martabar sarautun gargajiya bisa tsarin al'adu da dabi'u da aka gada.
Wannan mataki na zuwa ne kasa da mako guda bayan da wata kungiyar siyasa mai suna APC Patriotic Volunteers karkashin jagorancin Alhaji Usman Alhaji, ta soki yadda Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ke tafiyar da mulkinsa.
Tags:
Labarai