Rundunar 'Yan Sanda ta Jihar Kano na sanar da ci gaban da aka samu a bincike kan lamarin da ya haddasa kisan gilla ga CSP Baba Ali, wanda shi ne Divisional Police Officer (DPO) na karamar hukumar Rano, da kuma lalata dukiyoyi a lokacin da lamarin ya faru.
Bayan kammala bincike mai zurfi, rundunar ta gurfanar da mutum 29 a gaban Kotun Majistare mai lamba 20 da ke Nomansland, Kano, bisa zarge-zarge da suka shafi wannan mummunan lamari.
Mutum 14 daga cikin wadanda aka kama, ana zarginsu da aikata laifuka kamar haka:
- 
Hadin baki wajen aikata laifi 
- 
Tunzura jama'a 
- 
Kona dukiya da gangan 
- 
Taɓa kadarar wasu 
- 
Jikkata mutane da gangan 
- 
Sata 
Sunayen wadanda ake zargin sune kamar haka:
- 
Bala Yusuf 
- 
Bala Mohammed 
- 
Abdulrashid Ibrahim 
- 
Abdullahi Salisu Kere 
- 
Sadiq Buhari 
- 
Yunusa Adamu 
- 
Musa Minkaila 
- 
Mamuda Mohammed 
- 
Ismail Mamuda 
- 
Usman Shu'aibu 
- 
Musa Hassan Black 
- 
Abdulrashid Munkail 
- 
Umar Ado Nadada 
- 
Sabitu Abubakar 
Dukkansu sun fito nedaga karamar hukumar Rano, Jihar Kano.
Sauran mutum 15 kuma ana zarginsu da:
- 
Hadin baki wajen aikata laifi 
- 
Tunzura jama'a 
- 
Lalata dukiya 
Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da cewa za a tabbatar da adalci a wannan lamari, tana mai bayyana godiyarta ga jama’a bisa ta’aziyya, addu’o’i, goyon baya da fahimta da suka nuna yayin gudanar da bincike.
A karshe, rundunar na kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da guje wa daukar doka a hannunsu.
Rundunar za ta ci gaba da tabbatar da doka da oda da kuma kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin Jihar
