YAN SANDA SUN GURFANAR DA MUTANE 29 GABAN KOTU KAN KISAN GILLA DA AKE ZARGIN SUN AIKATA WA DPO NA RANO

Rundunar 'Yan Sanda ta Jihar Kano na sanar da ci gaban da aka samu a bincike kan lamarin da ya haddasa kisan gilla ga CSP Baba Ali, wanda shi ne Divisional Police Officer (DPO) na karamar hukumar Rano, da kuma lalata dukiyoyi a lokacin da lamarin ya faru.

Bayan kammala bincike mai zurfi, rundunar ta gurfanar da mutum 29 a gaban Kotun Majistare mai lamba 20 da ke Nomansland, Kano, bisa zarge-zarge da suka shafi wannan mummunan lamari.

Mutum 14 daga cikin wadanda aka kama, ana zarginsu da aikata laifuka kamar haka:

  • Hadin baki wajen aikata laifi

  • Tunzura jama'a

  • Kona dukiya da gangan

  • Taɓa kadarar wasu

  • Jikkata mutane da gangan

  • Sata

Sunayen wadanda ake zargin sune kamar haka:

  1. Bala Yusuf

  2. Bala Mohammed

  3. Abdulrashid Ibrahim

  4. Abdullahi Salisu Kere

  5. Sadiq Buhari

  6. Yunusa Adamu

  7. Musa Minkaila

  8. Mamuda Mohammed

  9. Ismail Mamuda

  10. Usman Shu'aibu

  11. Musa Hassan Black

  12. Abdulrashid Munkail

  13. Umar Ado Nadada

  14. Sabitu Abubakar

Dukkansu sun fito nedaga karamar hukumar Rano, Jihar Kano.

Sauran mutum 15 kuma ana zarginsu da:

  • Hadin baki wajen aikata laifi

  • Tunzura jama'a

  • Lalata dukiya

Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da cewa za a tabbatar da adalci a wannan lamari, tana mai  bayyana godiyarta ga jama’a bisa ta’aziyya, addu’o’i, goyon baya da fahimta da suka nuna yayin gudanar da bincike.

A karshe, rundunar na kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da guje wa daukar doka a hannunsu. 

Rundunar za ta ci gaba da tabbatar da doka da oda da kuma kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin Jihar

Previous Post Next Post